ibnhujjah
001 DA’AWAH BISA KOYARWAR ALQUR’ANI DA SUNNAH
FITOWA TA 1
MA’ANAR DA’AWAH
.
DA’AWAH: kalma ce ta larabci wadda tushenta ya ginu akan harufan Dalun, Ainun , da Wawun da Ta’un wato Da-A-Wa-Tu () Ma’anar Kalmar a harshe shine Kira, gaiyata ko hallarowa, wato ka Kirawo ko hallaro wani zuwa gareka ko zuwa wani bigire.
.
Alal misali, Alqur’ani mai girma yayi amfani da kalmar Da’awah a wajen hallaro da matattu daga kaburbura don tsarasu filin qiyama. ALLAH (SWT) Yana cewa acikin suratul Rum:
.
.
Ma’ana: “Kuma akwai daga ayoyinsa (alamomin Kudirarsa) tsayuwar sama da Kasa bisa umurninsa, sa’annan idan Ya Kira ku, Kira d’aya daga Kasa, sai gaku kuna fita.” [Rum:25]
.
Haka kuma acikin suratul Isra’i ALLAH (SWT) Yana cewa:
.
.
Ma’ana: “A ranar da zai Kira ku sai Ku amsa da gode masa, ku dinga zaton baku zauna ba, face lokaci d’an kad’an.” [Isra’i: 52]
.
A wad’annan ayoyi da suka gabata anyi amfani da Kalmar Da’awah da Ma’anarta Kira ko halartowa.
.
● DA’AWAH a fuskar shari’ah kuma ta kunshi Kiran bayi zuwa ga addinin ALLAH, wadda ta had’a da jawo mutane zuwa ga shiga Addinin Musulunci, Tunatarwa ga Musulmi da Ilimantar dasu akan Ka’idodi da Hukunce-Hukunce da ya tattara Aqeedah, Ibadah, Mu’amala, Zamantakewa, Tarihi, Mas’alar Al’umma da duk abunda Ya shafi rayuwar Musulmi a doron kasa.
.
● DA’AWAH ta tattaro tare da game dukkan nau’o’i na shiryar da bayi da shigar da su addinin musulunci, Umurni da kyakykyawan ayyuka da hani zuwa ga mummuna. Tunatarwa (Tazkir) da Nasiha a tsakanin musulmi don zaburar dasu bisa amfani da salon bushara da gargad’i da kuma buga misalai cikin Seera da Tarihin Al’ummomi da suka gabace mu. Akwai kuma kokarin tabbatar da tsayuwa akan umurni da hani a aikace ta hanyar ayyukan Hisbah da dai sauransu.
.
● DA’AWAH Kira ne don fahimtawa ko tunatarwa ga wad’anda ake kira zuwa gare su, bisa bukatar Jan hankalin su zuwa bautar ALLAH wajen kad’aita shi a bauta, Yi masa ‘da’a, bin umurninsa, barin haninsa da rayuwa bisa tafarkinsa. Don haka aikin Da’awah ya tattara yad’a Ilimin addinin musulunci ta hanyar tunatarwa ga wad’anda suka riga suka sani, gargad’i ga masu ketare iyakan ALLAH da jawo hankalin wad’anda basu fahimci ko kar6i kiran Musulunci ba.
.
Mu had’u a FITOWA TA 2 Inshaa ALLAH.