ibnhujjah
Malam ya cigaba da bayani akan TUSHEN DA’AWAH da cewa:
.
Wannan aiki na Da’awah tasirinsa bai taqaita ga d’an Adam ba, amma ya had’a har da al’ummar Aljanu. Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya kai da’awah har zuwa ga jama’ar Aljanu, sun saurare shi kuma sun taimake shi wajen yad’a wannan saqo zuwa ga al’ummomin su, kamar yadda Alqur’ani ya tabbatar da haka:
.
.
” Kuma lokacin da muka juya wadansu jama’a na Aljanu zuwa gareka suna sauraren alqur’ani, to a lokacin da suka halarce shi suka ce, kuyi shiru, sannan da aka kare, suka juya zuwa ga jama’arsu suna musu gargad’i Suka ce Ya mutanenmu, lallai mu munji wani littafin an sauqar dashi a bayan Musa, mai gaskatawa ga abunda ke gaba dashi, yana shiryarwa ga gaskiya da kuma zuwa ga hanya madaidaiciya Ya mutanen mu! Ku kar6awa mai kiran ALLAH kuma kuyi imani dashi, ya gafarta muku daga zunubanku, kuma ya tsirar daku daga azaba mai rad’ad’i.”. [Ahqaf:29-31]
.
Wasu malamai suna ganin ita Da’awah yanki ne na umurni da kyawawan ayyuka da hani ga munana. Masu wannan ra’ayi sun taqaita kalmar Da’awah bisa ma’anar IRSHAD wadda ke taqaita zuwa ga shiryar da mutane cikin addinin musulunci domin ALLAH (SWT) Yana cewa acikin littafinsa Mai girma:
.
.
” Kayi kira zuwa ga hanyar Ubangijinka (ALLAH) da hikima da wa’azi mai kyau kuma kayi jayayya dasu ga magana wadda take mafi kyau, Lallai ne Ubangijinka (ALLAH) shine mafi sani ga wanda ya 6ace daga hanyarsa, kuma shine mafi sani ga masu shiryuwa.” [Nahl:125]
.
Amma acikin bayanan da suka gabata da wad’anda zasu biyo baya, Kalmar Da’awah tana d’aukan dukkan abunda ya qunshi salo da hanyoyin isar da saqon addinin ALLAH ne zuwa ga bayinsa. Wallahu a’alam.
.
Mu had’u a FITOWA TA 5 Inshaa ALLAH.
WALLAFAR: SHEIKH ALIYU SA’EED GAMAWA.
.