ibnhujjah
005 DA’AWAH BISA KOYARWAR ALQUR’ANI DA SUNNAH
FITOWA TA 5
NAU’O’IN DA’AWAH
.
DA’AWAH kamar yadda bayani ya gabata, kalma ce wadda ta tattaro wata hanya da za’a isar da saqon Musulunci. Don haka akwai nau’o’in isar da da’awah ga bani adam bisa la’akari da irin mutanen da ake yiwa da’awar daga yanayin rayuwarsu da kuma salo ko yanayin isar musu da saqon.
.
Wato ana gabatar da da’awah ne bisa nau’in da ya dace da saqon da ake qoqarin isarwa ga al’umma, A bisa wannan ne aka umurci Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) da ya gabatar da aikin da’awah bisa nau’o’i ko salon-hikima, ta hanyar wa’azi mai kyau da kuma jayayya bisa Abunda yake mafi kyau a tsakanin wad’anda yake isarwa saqon.
.
Ana la’akari da irin saqon da ake isarwa da kuma wadanda ake buqatar isarwa zuwa gare su wajen amfani da wani nau’i na da’awah, wasu daga cikin nau’o’in da’awah sun had’a da IRSHAD ko shiryarwa zuwa ga addinin musulunci, Umurni da kyawawan ayyuka da hani zuwa ga munanan da dai sauransu.
.
SHIRYARWA ZUWA GA ADDININ MUSULUNCI (IRSHAD KO DA’AWAH)
.
Wannan aikin da’awah ne wadda ya qunshi isar da saqon musulunci ga al’ummomi ko mutanen da basu kar6e shi ba, daga cikin masu riqe da littafi ko kuma masu bautar wanin ALLAH da kuma wad’anda basu da wani addini baki d’aya, wannan shine jigon abunda aka aiko dukkan Annabawa da Mursalai akai. Wato qiran mutane su kad’aita ALLAH wajen bauta ta hanyar barin addinin qarya da suke bi, ko kuma domin su fahimci muhimmancin rayuwa cikin addini, ga wad’anda basu yi riqo ga ko wani addini ba kuwa sai ya zamanto hanyar jan hankalinsu zuwa ga addinin Musulunci.
.
A qarqashin wannan Nau’u na da’awah, tilas ayi la’akari da irin mutumin da za’a isar wa wannan saqo, Alal misali ya kamata a fahimci wane tafarki yake akai, menene fahimtarsa ga rayuwa da addini, ya iliminsa da wayewarsa yake da dai sauransu.
.
Malam Ahmad Deedat (ALLAH Yayi masa Rahama), malami ne da ya shahara wajen qiran mabiya addinin kirista zuwa ga musulunci, ya bada wani misali na yadda ake la’akari da yanayin irin mutumin da ake yiwa da’awah ayayin isar da saqon ALLAH, yayi nuni da yadda ALLAH (SWT) da kansa ya amsawa wasu rukunnan al’umma guda biyu a lokacin da suke da’awar jingina shi da ‘Ya’yaye ko suka yi masa tarayya awajen kad’aitakarsa.
.
Mu had’u a FITOWA TA 6 Inshaa ALLAH.