ibnhujjah
006 DA’AWAH BISA KOYARWAR ALQUR’ANI DA SUNNAH
FITOWA TA 6
Malam Ya cigaba da bayani akan NAU’O’IN DA’AWAH
.
Yace a lokacin da ma’abota littafi daga nasara suka ce ALLAH Yana da d’a ko d’ayan uku ne, sai Mabuwayi ya mai da musu da martani cikin kausasawa da nuna musu ta6ewarsu a inda yake cewa:
.
.
.
“Kuma suka ce mai rahama ya riki d’a! Lalla haqiqa kunzo da wani abu maigirman muni Sammai suna kusa su tsatstsage saboda shi, kuma Qasa ta kece kuma duwatsu su fad’i suna karyayyu. Domin sunyi da’awar d’a ga mai rahama.” [Maryam:88-91]
.
A wani wajen kuma ALLAH (SWT) Yace:
.
.
.
“Lallai haqiqa wad’anda suka ce ALLAH na ukun uku ne sun kafirta, kuma babu wani abun bautawa face ALLAH guda (d’aya), kuma idan badu hanu ga abunda suke fad’i ba haqiqa wata azaba mai rad’ad’i tana shafar wad’anda suka kafirta daga gare su.” [Ma’idah:73]
.
Amma awaje guda kuma yayinda mushirkan Makkah wad’anda suke rayuwa cikin jahiliyya, suka ce ALLAH ne yake da ‘Ya’ya mata su kuma suke da ‘Ya’ya maza, sai ALLAH Ya mayar musu da martani (bisa la’akari da ilimin su da wayewarsu) inda Yake cewa:
.
.
.
“Shin, kunga Lata da uzza? da manata na ukunsu? Ashe kune da ‘Da namiji, shi (ALLAH) kuma me da d’iya mace? Wannan fa ya zama rabo naqasashshe.” [Najmi:19-22]
.
Mu had’u a FITOWA TA 7 Inshaa ALLAH.