ibnhujjah
007 DA’AWAH BISA KOYARWAR ALQUR’ANI DA SUNNAH
FITOWA TA 7
Malam Ya cigaba da bayani akan NAU’O’IN DA’AWAH
.
A bisa wannan izina ne ya cancanta ga mai da’awah yayi la’akari da mutumin da yake kokarin kira zuwa ga addinin Musulunci, don za6in irin nau’in da’awah da zai yi ga wanda bashi da addini, tamkar maguzawa a kasar Hausa, bazai zama daidai da salo ko nau’in wa’azin da zaiyi wa ma’abota littafi ba. Su ma’abota littafi suna rike da wani saqo wadda suke zaton sauqaqqe ne daga sama, wanda yake d’auke da haqiqannin saqon ALLAH. Don haka ana tunkarar su ne ta fuskar jayayya (wato musayar ra’ayi) bisa hujjojin da suka yi riqo dasu da abunda yake Mafi kyau.
.
Zamu iya fahimtar haka idan muka yi la’akari da umurnin da ALLAH (SWT) ya baiwa Manzonsa (Sallallahu Alaihi Wasallam) na ya kira ma’abota littafi zuwa daidaitawa a tsakanin su, cikin abunda dukkanin su suke da’awah akai, ALLAH (SWT) Yana cewa:
.
.
“Kace: Yaku mutanen littafi! Ku taho zuwa ga kalma mai daidaitawa a tsakanin mu da ku; kada mu bautawa kowa face ALLAH, kuma kada mu had’a komai da shi, kuma kada sashenmu ya riqi sashe n Ubangiji baicin ALLAH, To idan sun juya baya sai ku ce: kuyi shaida cewa lallai ne mu masu sallamawa ne.” [Ali-imran:64]
.
A 6angare guda kuma shi wanda bai yadda da ko wani addini ba, za’a fara nuna masa virman ALLAH ne da ni’imomin da ALLAH yayi masa na samar dashi a matsayin d’an Adam ba dabba ba, ya kuma bashi lafiya da iskar da zai shaqa da dai sauran ni’imomin da ALLAH yayi mana, ALLAH (SWT) Yana cewa acikin littafinsa Maigirma:
.
.
“Ya ku mutane! Ku bautawa (ALLAH) Ubanginku wanda ya halicce ku, kuda wad’anda ke gabanninku, tsammaninku ku kare kanku! Wanda ya sanya muku kasa (ta zama) shimfid’a, kuma (ya sanyawa) sama gini kuma ya sauqar da ruwa daga sama, sannan ya fitar da abinci daga ‘Yayan itace game dashi saboda ku, saboda haka kada ku sanyawa ALLAH wash kishiyoyi, alhali kuwa kuna sane.” [Baqara: 21-22]
.
Mu had’u a FITOWA TA 8 Inshaa ALLAH.
WALLAFAR: SHEIKH ALIYU SA’EED GAMAWA.