ibnhujjah
009 DA’AWAH BISA KOYARWAR ALQUR’ANI DA SUNNAH
FITOWA TA 9
Malam ya cigaba da bayani akan UMURNI DA KYAWAWAN AYYUKA DA HANI ZUWA GA MUNANA.
.
Game da d’aid’aikun jama’a ALLAH (SWT) Ya siffanta muminai maza da mata da kasancewa masu aikin Umurni da kyawawan ayyuka da hani ga munana acikin littafinsa Maigirma inda Yake cewa:
.
.
“Kuma muminai maza da muminai mata sashensu maji6incin sashe ne, suna umurni da alkhayri kuma suna hani da abunda ba a so, kuma suna tsayar da Sallah, kuma suna bayar da zakka, kuma suna d’a-a ga ALLAH da Manzonsa, wad’annan ALLAH zai yi musu rahama, Lallai ALLAH shine Mabuwayi Mai hikima.” [Taubah:71]
.
Haka kuma hadisan Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) sun qarfafa wannan muhimmin aiki a tsakanin al’ummomin musulmai, Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) Yana cewa: “Duk wanda yaga wani abun Qi ya chanja shi da hannunsa, idan bazai iya ba ya chanja shi da harshensa, idan bazai iya ba yaqi shi a zuciyarsa wannan shine mafi raunin imani.” [Imam Muslim]
.
Har ila yau acikin wani hadisi ruwayar Ahmad, Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) Yana cewa: “Na rantse da wanda rai na ke hannunsa ko kuyi Umurni da kyawawan aiki, kuma kuma kuyi hani da munanan aiki ko kuma ya yi kusa ALLAH ya aiko muku da bala’i kuma idan kuka roqe shi bazai amsa muku ba.” [Imam Ahmad]
.
A qarqashin wannan nau’i na da’awah ana iya samun salo daban-daban na tunatarwa, Ana iya amfani da salon bushara (Jan hankali zuwa ga tanadin nau’o’in ni’ima da aka Samar don sakamako ga masu d’a-a da bin ALLAH), Gargad’i (na irin tanadin narkon azaba ga masu qetare iyakokin ALLAH), Bada labarun abubuwa da suka gabata na daga al’ummomin Annabawa da Alqur’ani ya ambatana da kuma rayuwar Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) da Sahabbansa da dai sauransu.
.
Mu had’u a FITOWA TA 10 Inshaa ALLAH.
WALLAFAR: SHEIKH ALIYU SA’EED GAMAWA.