ibnhujjah
016 DA’AWAH BISA KOYARWAR ALQUR’ANI DA SUNNAH
FITOWA TA 16
.
Malam ya cigaba da bayani game da HUKUNCIN DA’AWAH.
.
2● DA’AWAH A MATSAYIN FARDUL KIFAYAH:
.
Mafi yawan malamai sun raja’a akan cewa da’awah aiki ne na fardul kifayah wato aiki ne da ya wajaba akan dukkan musulmai, amma idan wasu yanki na jama’a zuka rungumi gabatar da wannan aiki, wajibcin yin aikin ya sauka akan sauran jama’a.
.
Wannan ra’ayi ya ginu ne bisa hujjar cewa: ALLAH (SWT) acikin ayar da yayi umurnin aikin da’awah, cikin suratul suratul Ali-imran cewa yayi: “Kuma wata jama’a daga cikinku ta kasance…” wato yankin jama’a ba kowa da kowa ba.
.
Ibnul Arabi yana da ra’ayin cewa fadin ALLAH cewa: “Za’a samu wasu al’umma daga cikinku” wanda ishara ne da wajibcin yin da’awah, yana nuni ne da kasancewar da’awah Fardul kifayah ne.
.
Haka ma Imam Ibnu Kathir acikin tafsirin wannan aya ya bayyana cewa: wannan aya tana nusar da cewa dole a samu wani rukuni daga cikin al’ummar musulmai da zasu rungumi aikin umurni da kyawawan aiki da hani zuwa ga munana, duk kuwa da kasancewa wannan aiki yana kan ko wani musulmi gwargodon iyawarsa.
.
Sheikh ibn Taimiyyah ya jaddada wannan ra’ayi, inda yake cewa: “umurni da kyawawan ayyuka da hani da munana bai wajaba akan kowa da kowa bisa kasancewarsa Fardul Ain ba, sai dai bisa kasancewarsa Fardul kifayah, wato wasu mutane zasu iya daukewa wa wasu, kamar yadda dalilai suka tabbata acikin alkur’ani…” Amma idan aka rasa samun wadanda zasu gabatar da wannan muhimmin aiki, wato aka bar aikin da’awah baki daya, to anan ukubar da zata biyo baya zata game kowa da kowa, kuma a wannan lokaci yin da’awah ya hau kan dukkan musulmai baki daya babu wanda zai fita.
Mu had’u a FITOWA TA 17 Inshaa ALLAH.