ibnhujjah
017 DA’AWAH BISA KOYARWAR ALQUR’ANI DA SUNNAH
FITOWA TA 17
.
Malam ya cigaba da bayani game da HUKUNCIN DA’AWAH
.
3● DA’AWAH A MATSAYIN AIKIN ALKHAIRI:
.
Duk da kasancewar aikin da’awah Fardul-kidayah ne, bisa mafi rinjayen magana a tsakanin malamai. Wato idan wasu suka rungumi aikin da’awah nauyin wajibcina ya saraya akan sauran jama’a, amma dumbin alkhairi dake cikin wannan aiki ya bayyana a fili karara.
.
Wasu malamai suna ganin babu yadda musulmi zai tsame hannunsa daga cikin aikin da’awah domin kawai wasu sun dauke masa wajibcin gabatar da wannan aiki. Domin duk da kasancewar aikin da’awah yana bukatar ilimi da fahimtar abunda ke kunshe cikin ilimin, amma ba a shardanta cewa sai mutum ya tara wani adadi na ilimi kafin yayi da’awah ba, asali ma ana bukatar kowa yayi kokarin isar da sakon musulunci gwargwadon iyawarsa, gwargwadon abunda ya fahimta, saboda fadin Manzon ALLAH (Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa: “Ku isar daga gare ni koda kuwa aya daya ce.” Sannan kuma ba a yarda musulmi ya jahilci addininsa ba, wajibi ne ko wani musulmi ga kowane musulmi yayi kokarin fahimtar dokokin addininsa, kuma ya kasance mai isar da abunda ya fahimta ga wasu idan halin yin hakan ya bayyana.
.
Mu sani cewa ALLAH (SWT) ya sanya abun banbamcewa a tsakanin musulmi mumini da Wanda yake munafuki abun zargi, bisa kasancewar shi mumini yana aikin umurni da kyawawan ayyuka da hani zuwa ga munana, alhali kuma munafuki babu abunda yake yi face akasin haka. ALLAH (SWT) Yana cewa:
.
.
“Kuma muminai maza da muminai mata sashensu majibincin sashe ne, suna umurni da alkhairi kuma suna hani daga abunda ba a so, kuma suna tsayar da Sallah, kuma suna bayar da zakkah, kuma suna da’a ga ALLAH da ManzonSa, wadannan ALLAH zai yi musu rahama, lallai ALLAH mabuwayi mai hikima me.” [Taubah:71]
.
Su kuma munafukai a nasu bangaren, ALLAH (SWT) ya siffanta su ne da ayyuka akasin na Muminai kamar haka:
.
.
“Munafukai Maza da munafukai mata, sashin su daga sashe, suna umurni da abun Ki, kuma suna hani daga alkhairi, kuma suna damkewar hannayen su, sun mance ALLAH, sai ya manta dasu, lallai ne munafukai sune fasikai.” [Taubah:67]