ibnhujjah
WAJIBI NE A KAN MALAMAI SU RIKA YIN UMURNI DA BIN UMURNIN ANNABI:
1. Wajibi ne a kan Malamai su tashi tsaye su rika umurtan Mutane da bin umurnin Manzon Allah mai tsira da amincin Allah cikin mas'alolin Aqidah, da Ibadah, da kuma Mu'amalah. 2. A duk inda aka tarar da cewa umurnin Manzon Allah ya saba da umurnin wani mutum da ake girmamawa a cikin Al'ummah, to dole ne a yi watsi da nasa umurnin a koma a bi umurnin shi Manzon Allah mai tsira da amincin Allah. Wannan shi ne Musulunci. 3. Al-Haafiz Bin Rajab ya ce a cikin littafinsa: Al-Hikamul Jadiiratu Bil Izaa'ah shafi na 12:- ))((. Ma'ana: ))Abin da yake wajibi a kan duk wanda umurnin Manzon Allah mai tsira da amincin Allah ya riske shi, ya kuma gane shi, to sai ya bayyana shi ga Al'ummah, ya yi musu nasiha, ya umurce su da bin umurnin shi; ko da hakan ya saba wa ra'ayin wani babba daga cikin Al'ummah; domin umurnin Manzon Allah mai tsira da amincin Allah shi ya fi cancantar a girmama a kuma yi koyi da shi a kan ra'ayin dukkan wani wanda ake girmamawa da ya saba wa umurninsa cikin sashin al'amura ta hanyar kure((. Allah muke roko da Ya sanya al'amuranmu cikin shiriya har kullum. Ameen.
Dr Jalo Jalingo.